Ma'anar Shi'anci a Gurin Ahlul Bait (A.S.)

Imaman Ahlul Bait (A.S.) babu wata himma da suka kasance da ita bayan sun kawar da kansu daga sa ran dawowar al'amarin al'umma gare su face himmar gyara musulmi da tarbiyyantar da su tarbiyyar da ta dace kamar yadda Allah Ta'ala yake so daga gare su. Don haka su kasance tare da duk wani da yake bin su kuma suka hakikance da rashin tona asirinsu suna matukar kokarinsu wajen koya masa hukunce-hukuncen Shari'a, suna cusa masa ilimin Muhammadiyya, suna sanar da shi abinda yake nasa da kuma wanda yake kansa.
Ba sa daukar mutum cewa mabiyansu ne, daga Shi'awansu ne sai dai idan ya kasance mai bin Allah, mai nesantar son zuciyarsa mai riko da koyarwarsu da shiryarwarsu.
Ba su daukar cewa soyayya gare su kawai ta wadatar wajen tsira, kamar yadda wasu ke gamsar da kansu daga cikin masu kage da bin sha'awace - sha'awace, kuma wadanda ke neman uzurin kangarewa biyayya ga Allah su Imamai, ba sa daukar soyayya gare su da biyayya ga shugabancinsu tsira ne sai dai idan an hada da kyawawan ayyuka, an kuma yi halin biyayya gare su da gaskiya da rikon amana, da tsoron Allah da takawa.
"Ya Khaisama ka isar ga mabiyanmu[1]cewa ba za mu dauke masu komai ba daga Allah face da aiki, kuma su ba za su samu soyayyarmu ba sai da tsoron Allah, kuma lalle mafi hasarar mutane ranar Alkiyama shi ne wanda ya siffanta adalci sannan kuma ya saba masa zuwa wani abu da ba shi ba."2
Sai dai su suna son mabiyansu ne su zamanto masu kira zuwa ga gaskiya, masu shiryarwa zuwa ga alheri da rabonta kuma suna ganin cewa kira a aikace ya fi kira da harshe isarwa "Ku kasance masu kiran mutane zuwa ga alheri ba da harsunanku ba, su ga kokari da gaskiya da tsoron Allah daga gare[3]ku.
A halin yanzu za mu kawo maka wata muhawara da ta gudana tsakaninsu da wasu daga cikin mabiyansu domin ka san tsananin himmatuwarsu da kwadayinsu a kan gyara dabi'un mutane:
1- Muhawarar Abu Ja'afar Bakir (A.S.) da Jabir Ja'afi:
"Ya Jabir ashe wanda yake sanya wa kansa cewa shi Shi'a ne zai wadantu kawai da soyayya gare mu mu Ahlul Bait? To wallahi babu wani Shi'a mai bin mu sai dai wanda yaji tsoron Allah ya bi Shi."
Su ba a kasance an san su ba sai da kankan da kai da tsoron Allah, da amana da yawan zikirin Allah, da azumi, da salla, da bin iyaye, da alkawari ga makwabta fakirai da matalauta da mabarsa da marayu tare kuma da gaskiyar magana da karatun Alkur'ani da kame harshe daga ambaton mutane sai dai da alheri, kuma sun kasance aminan jama'arsu a kan al'amura.
Saboda haka ku ji tsoron Allah kuma ku yi aiki saboda abinda yake ga Allah, babu wata dangantaka tsakanin Allah da wani, mafi samun soyayya a gurin Allah a cikin bayi shi ne mafificinsu a tsoron Allah da kuma mafificinsu a aiki da biyayyarsa."
Ya Jabir Wallahi ba mu kusanta ga Allah sai dai da da'a, kuma babu kubutarwa daga wuta a gare mu, kuma babu wata hujjar wani a kan Allah, duk wanda ya kasance mai biyayya ga Allah to shi masoyi ne gare mu duk wanda ya kasance mai sabo ne ga Allah to shi makiyi ne gare mu, kuma ba a samun jagorancin mu sai da aiki da tsoron [4] Allah."
2- Muhawarar Abu Ja'afar (A.S.) da Sa'id Bin Hasan:
Abu Ja'afar (A.S.): " Ashe dayanku zai zo ga dan'uwansa ya iya hannunsa a jakarsa ya dauki abinda yake so bai cire shi ba".
Sa'id: Ban san wani da haka ba a cikinmu.
Abu Ja'afar (A.S.): " To babu kome ke nan."
Sa'id: " To halaka ke nan."
Abu Ja'afar (A.S.): " Mutane ba a ba su mafarkinsu ba ke nan tukunna."[5]
3- Mahawarar Abu Abdullah Sadik (A.S.) da Abi Sabahi Kanani:
Kanani ya ce ga Abi Abdullahi "Abinda muke gamuwa da shi daga mutane game da ku."
"Menene abinda kuke gamuwa da shi daga mutane?"
Kanani: Bai gushe ba magana na gudana tsakaninmu da mutane ya ce dan Ja'afariyya ne mugu.
Abu Abdillahi: "Mutane na aibata ku a kaina ?"
Kinani: E!
Abu Abdillah: Karanci mai bin Ja'afar a cikinku ya yawaita! Sahabbaina kawai su ne wanda tsoron Allah gare Shi ya yawaita, kuma ya yi aiki ga mahaliccinsa kuma ya tsammaci ladansa. Wadannan su ne sahabbaina."[6]
4- Abi Abdillah (A.S.) yana da wasu maganganu game da wannan al'amari, daga ciki za mu kawo abinda ke biye:
a- "Baya daga cikinmu -babu karama kuma- wanda ya kasance a cikin wani birni da adadin dubu dari ko fiya da haka, kuma wani a cikin wannan birni ya zamanto ya fi shi tsoron Allah."[7]
b- "Mu ba ma kidaya mutum mumini har sai ya zamanto mai biyayya ga dukkan umarninmu da kuma nufi, ku ji ku sani daga cikin bin umarninmu da kuma nufinsa ne tsoron Allah, don haka ku zamanto kun kawata da Shi, Allah Ya rahamshe[8] ku."
c- "Wanda mata masu tsari basu magana game da tsanteninsa ba ya daga cikin Shi'awanmu, haka kuma wanda ya kasance a cikin karamin gari mai adadin mutane dubu goma, daga halittun Allah daya a cikinsa ya fi shi tsoron Allah."[9]
d- "Shi'awan Ja'afar, mabiyansa, kawai su ne: wanda ya kame cikinsa da farjinsa kokarinsa ya tsananta, kuma ya yi aiki ga mahaliccinsa ya sa rai da sakamakonSa kuma ya ji tsoron ukubarSa. To idan ka ga wadannan to wadannan su ne Shi'awan Ja'afar."[10]


[1]Al- Kafi Juzu'i na 2 shafi na 64 hadisi na 12.
[2]
[3] Al Kafi Juzu'i na 2 shafi 40 hadisi na 2.
[4]Da wannan ma'anar ne Amirul Muminin Aliyu Bin Abi Talib (A.S.) yake cewa "Lalle hukuncinsa a kan mazauna sama da mazauna kasa duk tabbas daya ne, kuma babu wani tsakanin Allah da wani daga zikin bayinsa kan halatta gewayen haramiyyarsa ga halittu." Nahjul Balagha Khutuba ta 192.
[5]Al-kafi Juzu'i na 2 shafi na 139 hadisi na 13.
[6]Al- Kafi Juzu'i na 2 shafi na 62 hadisi na 6.
[7] Al-Kafi Juzu'i na 2 shafi na 63 hadisi na 10.
[8] Al-Kafi Juzu'i na 2 shafi na 63 hadisi na l3.
[9] Al-Kafi Juzu'i na 2 shafi na 64 hadisi na 15.
[10] Al-Kafi Juzu'i na 2 shafi na 183 hadisi na 9.