Addu'o'in Sahifatus
Sajjadiyya
Bayan aukuwar
al'amarin Karbala mai ban takaici da kuma kame ragamar shugabancin al'ummar
musulmi da Banu Umayya suka yi kuma suka dulmuya a cikin danniya, suka yi
dumu-dumu da jinin mutane, sa'an nan suka yi watsi da koyarwar addini sai Imam
Zainul Abidin (A.S.) wato Sayyiddus Sajidin Ya zauna a gidansa yana bakin ciki
da jin takaici. Yana gida babu wani mai kusatarsa kamar yadda ba zai iya yada
wa mutane abinda ya wajaba a kansu ko ya kamata su sani ba na addini.
Don haka ala tilas ya zama babu makawa gare shi
ya dauki salon addu'a wanda muka ambata da cewa yana daga cikin hanyoyin
koyarwa da ladabtar da zukata ya rike shi a matsayin hanyar yada koyarwar
Alkur'ani da ladubban musulunci da kuma sanar da tafarkin Ahlul Bait (A.S.) da
kuma hanyar cusa wa mutane ruhin addini da zuhudu da kuma abinda ya wajaba na
daga gyaran zukata da kuma kyawawan dabi'u.
Wannan hanya ce da ya fare ta a fakaice don
koyar wa mutane ba tare da ya jawo hankalin azzaluman Shugabanni da ke matsa
masa ba, ba kuma za su iya kafa masa wata hujja ba. Don haka ne yawancin
Wadannan addu'o'i masu zurfi an tattara wadansunsu a littafin Sahifatus
Sajjadiyya wanda ake yi wa lakabi da "Zaburar Zuriyar Muhammadu
(S.A.W.A)" salonta da manufofinta sun zo da siga da salon Larabci mafi
daukaka, da mafi ingancin asirran tauhidi da Annabci da kuma mafi ingancin
hanyar koyar wa da kyawawan dabi'u ababan yabo da kuma ladubban musulunci.
Wadannan addu'o'in sun shafi al'amura
dabam-daban ne na tarbiyya ta addini ta shafi koyarwar addini da kyawawan
dabi'u ta hanyar addu'a, ko kuma addu'a ce amma da salon koyar da addini da
kuma kyawawan dabi'u. Alal hakika bayan Alkur'ani da Littafin Nahjul Balagha
wannan Littafin addu'o'in shi ne salon bayanin Larabci mafifici kuma mafi
daukakar mashayar manufar sanin Ubangiji da kyawawan dabi'u. Daga cikinsu akwai
wanda ke sanar da kai yadda zaka daukaka Allah kuma ka tsarkake Shi, kana kuma
ka yi hamdala ka yi wa Allah godiya, daga bisani ka tuba gareShi.
Daga ciki akwai wadda ke sanar da kai yadda
zaka yi zance da Allah, kuma ka kadaita da kai ga Ubangijinka kana mai bayyana
Masa asirinka sannan ka zabura zuwa gare Shi.
Daga cikinta akwai
wadanda ke shimfida maka ma'anar Salati ga Annabi (S.A.W.A) da Manzannin Allah
da zababbunSa daga cikin halittunSa da yadda za ka yi da Shi.
Daga cikinsu akwai
wadanda za su fahimtar da kai abinda ya dace ka bi iyayenka da shi.
Kazalika akwai wadanda ke maka sharhin hakkokin
Uba a kan dansa, ko kuma hakkokin makwantai, ko wadanda kuke ciki daya, ko
hakkokin musulmi baki daya, ko hakkokin matalauta a kan mawadata da kuma akasin
haka.
Daga cikin addu'o'in akwai wanda zai fadakar da
kai kan abinda ya wajaba na basussukan mutane akan ka, da kuma abinda ya kamata
ka aikata akan lamurran kafi da tattalinsu, haka na da abinda ya kamata kayi
mu'amala da shi tsakaninka da masu hulda da sauran abokanka da kuma mutane baki
daya, har yanzu akwai wanda zai gwada maka irin mutanen da za ka iya hulda da
su domin amfanin kan ka.
Daga cikinsu akwai wadanda suke hado maka
dukkan manyan halayen kwarai da za sa su iya zama cikakken tsari na ilimin
kyautata dabi'u.
Daga cikinsu akwai wadanda za su koya maka
yadda za ka yi hakuri a kan
munanan abubuwa da ke aukuwa da kuma yadda za ka yi yayin da kake ciwo da kuma
yayin da kake kalau.
Daga cikinsu akwai wadanda ke maka sharhin
wajiban sojojin musulunci da wajiban mutane dangane da su... da dai sauran
wadannan da kyawawan dabi'u abin yabo suke farlanta su, duk ta hanyar addu'a
kawai.
Bayyanannun al'amuran da ke fitowa fili a
addu'o'in Imam sun kasu kamar haka:- Na farko:
Sanin Allah Ta'ala da girman kudurarSa da
bayanin kadaita Shi, da tsarkake Shi, da mafi dacewar ma'anoni na ilimi, wannan
kuwa yana maimaituwa ne a kowace addu'a ta salo dabam-daban kamar yadda kake
karantawa a addu'a ta farko:
"Godiya
ta tabbata ga Allah na farko wanda babu wani na farko da Ya kasance kafin Shi,
Na karshen da babu wani na karshe da zai kasance baicin Shi Wanda idandunan
masu gani suka gaza ganinSa, wahamce - wahamcen masu sifance - sifance kuma
suka gajiya wajen siffanta Shi. Ya fari halittu da kudurarSa a farkon farawa Ya
kuma kago su kamar yadda Ya so kagowa."
Karanta ma'ana ta farko da kyau kuma ka yi
tunani a kanta za ka tsarkake Allah Ta'ala daga kasancewarSa wani ya zamanto ya
gewaye da gani ko da wahami, da kuma ginin ingancin ma'anar halitta da kuma
halittar duniya baki daya.
Daga nan kuma ka karanta wani salon wajen
bayyana kudurar Allah Ta'ala da yin tuntuni a addu'a ta 6:
"Godiya
ta tabbata ga Allah wanda Ya halitta dare da rana da karfinSa, Ya rarrabe
tsakaninsu da kudurarSa, Ya sanya ga kowane daga cikinsu su biyun iyaka
ayyananniya, Yana shigar da kowane daya daga cikinsu a cikin dan'uwansa a
cikinsa da kaddarawarsa ga bayi a cikin abinda yake ciyar da su kuma Yake sanya
su su girma. Don haka Ya halitta musu dare ne domin su huta wahalar kaiwa da
komowa da dawainiya kuma Ya sanya shi sutura da za su suturtu da kwanciyarsu da
natsuwarsa domin hakan ya zama musu wartsakewa da kara samun karfi kuma domin
su kara samun jin dadi da sha'awa."6 Har zuwa karshen abubuwan
da ya ambata na fa'idar halittar rana da dare da kuma abinda ya kamata mutum ya
yi godiyarsa daga wannan ni'imar.
A wani salon kuma na bayanin dukkan al'amura ga
Allah Ta'ala suke za ka karanta a addu'a ta 7 cewa:
"Ya
wanda da Shi ne kulle-kullen munanan abubuwa ke suncewa, Ya wanda da shi ne
kaifin tsanani ke duskurewa, Ya wanda daga gare Shi ake rokon mafita zuwa
tsantsan sauki mawuyatan al'amura na rusunawa ga kudurarKa, sabubba kuma sun
samu ne da tausasawarKa, kaddarawarKa kuma ta gudana ne a bisa iradarKa, su da
iradarKa suke bin umarninKa, kuma masu umartuwa da maganarKa ne kuma da
iradarKa ne suke tsawatuwa da haninKa."
Na Biyu:
Bayani game da falalar Allah ga bawanSa, da kuma gazawar bawa wajen bayar da
hakkin Allah Ta'ala kome abinda ya yi na da'a da ibada kuwa da kuma yankuwa don
juyawa ga Allah kamar yadda kake karantawa a addu'a ta 37:
Ya Allah lalle babu wani da zai kai ga matukar godiya gare Ka face wata
kyautatawarKa ta same shi wadda za ta sake lizimta masa wata godiyar. Kuma ba
ya kaiwa ga matukar da'arKa koda kuwa ya dage face ya gaza yin yadda Ka cancanta a kan falalarKa,
Mafificin mai godiya gare Ka a bayinka ya gaza a kan godiyarKa, kuma mafi bautarsu mai kwauro ne a
bautarKa."
Saboda girman ni'imomin Allah Ta'ala a kan bawanSa bawan ya yi kadan ya ba da hakkinSa
komai kokarin da ya yi kuwa.
To yaya kuma idan har ya sabe Shi yana mai
tsaurin kai, yayin nan kuma ba zai taba iya kankare sabo koda guda daya ba,
kuma wannan shi ne abinda yankin addu'ar da ke biye a addu'a ta 16 ke nunawa:
"Ya
Ubangijina idan da zan yi kuka har fatar idona ta zagwanye, kuma na yi kururuwa
har muryata ta dushe, kuma na tsaya gare Ka har kafafuwana su tsattsage kuma na
yi maka sujada har kwayar idandunana su faffado, kuma na ci turbayar kasa duk
tsawon rayuwata kuma na sha ruwan toka har zuwa karshen zamanina sa'an nan na
yi ta ambaton ka duk tsawon wannan lokacin har sai harshena ya gaza, sa'an nan
kuma na zama ban taba daga ganina na dubi sama ba don jin kunyar ka, duk wannan
ba zai wajabta shafe mini mummunan aiki daya daga miyagun ayyukana ba."
Na uku:
Sanar da lada da ukuba da aljanna da wuta da
kuma cewa ladan Allah dukkaninsa kyauta ce kawai kuma bawa ya cancanci azaba ne
da zarar aikata sabo guda daya kawai da ya yi tsaurin idon aikatawa, Kuma Allah
na da hujja a kansa game da haka.
Kuma dukkan addu'o'in Sahifatus Sajjaddiya na
ambata wannan ukubar mai tasiri domin samar wa zuciya tsoron ukubar Allah
Ta'ala da sanya mata sa tsammani da ladan Allah Ta'ala. Dukkanta shaida ce a
kan haka ta salo mafifici da ke sa wa zuciya mai tuntuni tsoro da firgita kan
kama hanyar sabo, wato kamar abinda za ka karanta a addu'a ta 46:
Hujjarka tabatacciya ce ba za ta shafu ba,
Shugabancinka tsayayye ne ba ya ciruwa, don haka tsananin azaba madawwami ya
tabbata ga wanda ya nesance Ka, tabewar tozartuwa ta tabbata ga wanda ya
karkace daga gare Ka, tsiyacewar tsiyata ta tabbata ga wanda ya rudu ya bar Ka,
jujjuyawarsa a azabarKa ta yawaita, taraddudinsa a cikin ukubarKa ya yawaita,
bukatarsa ga samun budi ta kai matuka, debe tsammaninsa ga samun mafita mai
sauki ya tsawaita, Adalci ne daga hukuncinKa ba Ka zalunci a cikinsa, da kuma
yin daidai a hukuncinKa ba ya kaucewa, lalle Ka bayyanar da hujjoji kuma Ka
jarraba uzurori."
Da kuma kamar yadda kake karantawa a addu'a ta
31.
"Ya
Allah Kaji kan kadaitakata a gaban Ka, da kidimewar zuciyata
daga tsoronKa da firgicewar gabobina don haibarKa, kuma lalle Ya Ubangijina
zunubina ya sanya ni a matsayin kaskanci a gurinKa. Idan har na yi shiru babu
wani da zai yi magana a madadina, idan kuma na nemi a cece ni to ni ban
cancanci ceto ba."
Da kuma wadda kake karantawa a addu'a ta 39:
"Domin
Kai idan har Ka saka mini daidai wadaida to za Ka halakar da ni. Idan kuma ba Ka
lullube ni da rahamarKa ba to za Ka halakar da ni. Kuma ina rokon Ka Ka dauke
daga zunubina wanda nauyinsa ya dankare ni. Kuma ina neman taimako da kai a kan
abinda nauyinsa ya riga ya makure ni. Don haka Ka yi dadin tsira ga Muhammadu
da zuriyarsa. Kuma Ka ba wa raina kansa saboda zaluncinsa ga ni kaina, kuma Ka
wakilta rahamarKa wajen daukar nauyina."
Na Hudu:
Jan mai addu'a
zuwa ga madaukakan matsayin ayyuka da kebantattun siffofi domin kyautata
ruhinsa da tsarkake zuciyarsa ta hanyar karanta wannan addu'ar kamar yadda kake
karantawa a addu'a ta 20:
"Ya Allah Ka kammala min niyyata da
tausasaawarKa, kuma Ka inganta mini niyyata da abinda ke gare Ka, kuma Ka gyara
mini abinda ya baci daga gare ni da kudurarKa, ...Ya Allah Ka yi dadin tsira ga
Muhammadu da zuriyar Muhammadu Ka jiyar mini dadi daga shiriya ingantacciya
wadda ba zan taba neman musayenta ba, da kuma hanya ta gaskiya wadda ba zan
taba karkacewa daga kanta ba, da kuma niyyar shiriya daba zan taba kokwanto a
kanta ba.
... Ya Allah Kada Ka bar wani hali da yake aibi
gare ni face Ka gyare shi, ko kuma wani laifi da za a zarge ni da shi illa Ka
kyautata shi. Ko kuma wani halin karimci da yake tauyayye gare ni har sai Ka
cika Shi."
Na Biyar:
Sanya wa mai karanta addu'ar mutumta mutane da
rashin kaskantar da su, da kuma cewa kada ya sanya bukatarsa a gurin wani ba
Allah ba da kuma cewa kwadayin abinda ke hannun mutane na daga cikin mafi
kaskancin abinda mutum zai siffantu da shi kamar yadda kake karantawa a addu'a
ta 20:
"Kuma
kada Ka fitine ni da neman taimakon wani ba Kai ba idan na matsu da kuma kankan
da kai don tambayar wani ba Kai ba idan na bukata, da kuma mika wuya gaba ga
wanda ba Kai ba idan na tsorata, kada na zamanto na tozarta da hanawa da kau da
kai ta yin haka."
Da kuma misalin addu'a ta 28:
"Ya
Allah ni na tsarkake niyyata gare Ka duka, kuma na juyo zuwa gare Ka baki daya,
kuma na juyar da fuskata daga dukkan ma'abucin taimakonKa, Na juyo da
al'amarina daga dukkan wanda ba zai taba wadatuwa ya bar falalarKa ba, kuma na
gane cewa bukatar mabukaci zuwa ga wani mabukacin wautar ra'ayinsa ne kuma
bacewar hankalinsa ne."
Kazalika addu'a ta 13:
"
Duk wanda ya yi kokarin magance rashinsa ta gurinKa kuma ya yi kokarin raba
kansa da talauci da taimakonKa to lalle ya nemi abin bukatarsa a gurin da ake
tsammani, kuma ya zo wa bukatarsa ta gurin da ya dace. Kuma duk wanda ya juya
da bukatarsa zuwa ga daya daga cikin halittunKa, ko kuma ya sanya shi sababin
cim mata ba kai ba , to lalle ya jawo wa kansa hani kuma ya cancanci kubucewar
kyautatuwa daga gare Ka."
Na Shida:
Koya wa mutane wajabcin kiyaye hakkokin wasu,
da taimaka musu da tausasawa gare su, da rangwame ga junansu, da sadaukarwa da
tabbatar da ma'anar 'yan'uwantakar musulunci, kamar yadda kake karantawa a
addu'a ta 38:
"
Ya Allah ni ina mai neman uzuri daga gare Ka a kan dukkan wani da aka zalunta a
gabana amma ban taimake shi ba, da kuma wani kyakkawan abu da aka kwararo mini
shi amma ban yi godiyarsa ba da kuma duk wani mabukaci da ya roke ni amma ban
ba shi ba, da kuma daga hakkin duk wani ma'abucin hakki da ya hau kaina daga
muminai amma ban cika mashi ba, da kuma daga dukkan wani aibi na mumini da ya
bayyana gare ni amma ban suturce shi ba. "
Lalle wannan irin neman uzuri yana daga cikin
mafi bayyanar abinda zai fadakar da zuciya zuwa ga abinda aikata shi ya kamata
na wadannan kyawawan dabi'u madaukaka da Ubangiji Ya yarda da su.
A addu'a ta 39 akwai abinda ke bada karin haske
a kan haka tare da lizimtar da kai yadda za ka yafe wa wanda ya munana maka
yana kuma gargadinka game da yin ramuwar gayya yana kuma daukaka zuciyarka zuwa
matsayin tsarkakuwa:
"Ya
Allah duk wani bawa da ya cutar da ni da wani abu da ka haramta, kuma ya keta
mini abinda Ka riga Ka hane shi a kai, kuma ya mace da zaluntata ko kuma ya
auku a kaina daga gare shi yana rayayye, to Ka gafarta masa abinda yayi mini,
Ka yafe masa abinda ya riga ya aukar ya wuce daga gare ni, kada ka dakatar da
shi da tambaya a kan abinda ya aikata a kaina, kuma kada ka tona asirinsa a kan
abinda ya aikata a kaina, kuma ka sanya rangwamen da na yi masa na afuwa gare
su da kuma sallamawar da na yi musu na daga sadaka gare su ya zama sadakar masu
sadaka, kuma mafi kololuwar sadarwar ma'abuta kusanci gare Ka. Kuma Ka musanya
mini afuwata gare su da afuwarKa, da kuma addu'ata gare su rahamarKa, har ya
zamanto kowane daya daga cikinmu ya rabonta da falalarKa ya kuma samu tsira
saboda baiwarKa."
Al'ajabin wannan yankin addu'ar da yawa yake,
kyawun tasiri da shigarta zuciyar zababbu ya yawaita, don fadakar da su a kan lizimtar kyakkyawar niyya da dukkan mutane, da
neman rabbonta ga kowa da kowa hatta ma wanda ya zalunce shi ya ketare masa
haddi.